Pep Guardiola ya musanta jita-jitar cewa zai bar Manchester City a ƙarshen kakar wasa, yana mai cewa har yanzu yana nan daram a kulob ɗin duk da rahotannin da ke alaƙanta shi da ficewa.

A cewar BBC Sport a ranar Talata, wasu rahotanni sun bayyana cewa City na yin shirye-shiryen cikin gida dangane da yiwuwar tafiyar Guardiola bayan wasan Premier League da suka buga da Aston Villa a ranar Lahadi, inda tsohon mataimakin koci Enzo Maresca ke kan gaba wajen maye gurbinsa.

Sai dai Guardiola ya yi gaggawar rage ƙarfin waɗannan jita-jitar yayin taron manema labarai kafin tafiyar City zuwa Bournemouth.

“Sau da yawa na faɗa cewa har yanzu ina da shekara guda a kwantiragina,” in ji Guardiola lokacin da aka tambaye shi game da makomarsa a kulob ɗin.

Ɗan asalin Spain ɗin, wanda har yanzu yake da saura shekara guda a kwantiraginsa a filin wasa na Etihad, ya kuma musanta cewa wasan Talata na iya kasancewa wani ɓangare na bankwana da magoya baya.

“Ina nan, kuma ina da kwantiragi,” in ji shi.

An kuma tambayi Guardiola kan rahotannin cewa City na iya karrama shi ta hanyar sanya sunansa ga sabon ɓangaren North Stand idan ya bar kulob ɗin a wannan bazarar.

“A’a, a’a, a’a, ban san komai game da hakan ba,” in ji Guardiola