Ministar harkokin wajen Najeriya ta bayyana cewa ƙasar ba za ta amince da ci gaba da cin zarafi da wulakanta ’yan Najeriya a South Africa ba.

Ta bayyana hakan ne yayin tattaunawa kan dangantakar da ke tsakanin ƙasashen biyu da kuma ƙalubalen da wasu ’yan Najeriya ke fuskanta a ƙasar.

Ojukwu ta jaddada cewa gwamnatin Najeriya za ta ci gaba da kare mutunci da haƙƙin ’yan ƙasarta a duk inda suke a duniya, tare da kira da a mutunta su kamar sauran al’ummomi.

Kalaman nata na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun koke-koke kan hare-hare, cin zarafi da sauran matsalolin da wasu ’yan Najeriya ke fuskanta a South Africa.