Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da sabbin ministoci biyu, inda ya naɗa Joseph Tegbe a matsayin Ministan Lantarki, yayin da Sola Enikanolaiye ya zama Ƙaramin Ministan Harkokin Waje.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, tare da halartar iyalan sabbin ministocin da manyan jami’an gwamnati.

Joseph Tegbe, ɗan asalin Ibadan da ke Jihar Oyo, ƙwararren masani ne a fannin sauye-sauyen tattalin arziki, harkokin kuɗi da tsarin hukumomi. Ya shafe sama da shekaru 35 yana aiki a gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu, inda ya taka muhimmiyar rawa a fannoni daban-daban na ci gaban tattalin arziki.

A nasa ɓangaren, Sola Enikanolaiye, ɗan asalin Igbagun da ke Jihar Kogi, gogaggen jami’in diflomasiyya ne da ya yi fice a harkokin hulɗar ƙasa da ƙasa. Ya kammala karatun digiri na farko a Ahmadu Bello University da sakamako mai kyau, sannan ya samu digiri na biyu a fannin Dokar Ƙasa da Harkokin Diflomasiyya daga University of Lagos.

An bayyana sabbin ministocin a matsayin ƙwararru masu gogewa da ilimi mai zurfi, waɗanda ake sa ran za su bayar da gudunmawa wajen inganta ayyukan gwamnati da ci gaban ƙasa a fannoni daban-daban.