Atiku ya yabawa sojojin Najeriya kan ceto mutum 360 daga hannun Boko Haram a Borno

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yaba wa dakarun sojin Najeriya bisa nasarar da suka samu wajen kuɓutar da mutum 360 da aka sace a ƙauyen Ngoshe da ke Jihar Borno.

Rahotanni sun ce an gudanar da aikin ceton ne a yankin Dutsen Mandara, inda mayaƙan Boko Haram suka tsare mutanen bayan wani hari da suka kai kan sansanin soji da ke Ngoshe.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Litinin, Atiku ya bayyana farin cikinsa kan nasarar aikin, yana mai cewa hakan ya kawo sauƙi ga waɗanda aka kuɓutar da kuma iyalansu da suka shafe watanni cikin damuwa tun bayan sace su a watan Maris.

“Atiku ya ce ya yi matuƙar farin ciki da jin labarin kuɓutar da mutum 360 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a Ngoshe, Jihar Borno,” in ji sanarwar.

Sai dai ya jaddada cewa duk da wannan gagarumar nasara, har yanzu Najeriya na fuskantar ƙalubalen rashin tsaro da suka haɗa da ayyukan ta’addanci da hare-haren ‘yan bindiga a sassa daban-daban na ƙasar.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma yabawa rundunar soji da sauran hukumomin tsaro da suka taka rawa wajen gudanar da aikin, yana mai cewa jajircewarsu da sadaukarwarsu ne suka ba da damar ceto mutanen cikin nasara.

Atiku ya bayyana cewa yana da yakinin cewa idan aka ci gaba da samar wa jami’an tsaro kayan aiki na zamani tare da ingantaccen shugabanci da goyon baya, za su iya shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar Najeriya.