Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump ya ce ya bayyana matakin ne bayan wayar da ya yi da shugabannin ƙasashen Larabawa a karo daban-daban da kuma Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.

Shugaban na Amurka ya ce cikin yarjejeniyar da aka cimma akwai batun sake buɗe mashigar Hormuz.

Ya ce yanzu ana tattauna matakin ƙarshe na yarjejeniyar kuma nan ba da jimawa ba za a sanar da abin da aka cimma.