Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta soke wasu sassan jadawalin zaben 2027 da Hukumar INEC ta fitar, bayan wata kara da jam'iyyar YP ta shigar.
Mai shari'a Mohammed Umar ya ce wasu wa'adin da INEC ta kayyade wa jam'iyyun siyasa sun saba wa Dokar Zabe ta 2026, musamman batun lokacin gudanar da zaben fidda gwani, gabatar da sunayen 'yan takara, janye takara da maye gurbin 'yan takara.
Kotun ta bayyana cewa INEC ba ta da ikon rage ko sauya wa'adin da doka ta tanada, tare da cewa ba za ta iya kayyade karshen yakin neman zabe ko fitar da jerin 'yan takara ta hanyar da ta saba wa doka ba