Kungiyar malaman makarantun sakandare da firamare ta kasa (NUT) ‎, ta bayyana matukar damuwa kan yadda hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane ke kara kamari a makarantu, tana mai gargadin cewa hakan na iya tilasta malamai janye ayyukansu idan gwamnati ba ta dauki matakin gaggawa ba.


‎A wata sanarwa da shugaban kungiyar na kasa, Audu Amba, tare da babban sakataren kungiyar suka sanyawa hannu, kungiyar ta ce makarantu sun daina zama wuraren koyarwa cikin kwanciyar hankali, inda suka koma filin hare-haren ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda.

‎Kungiyar ta bayyana hare-haren a matsayin abinda ya jefa malamai, dalibai, iyaye da mazauna yankunan da abin ya shafa cikin tsananin firgici da tashin hankali.


‎Kungiyar ta bukaci jami’an tsaro su gaggauta daukar matakan ceto wadanda aka sace tare da tabbatar da tsaron makarantu a fadin kasar nan.