Ministan Harkokin Wajen Syria ya ce Damascus na sa ran za a sake dawo da tattaunawa da Isra’ila kan yarjejeniyar tsaro nan ba da jimawa ba.

Kwanaki kaɗan bayan da Isra’ila ta kai harin sama kan wani sansanin sojan Syria, Asad Shaibani ya jaddada a wata hira da Reuters cewa babban abin da Damascus ke son cimmawa a yanzu shi ne dakatar da hare-haren Isra’ila.

A cewarsa, domin samun ci gaba a wannan fanni, ya zama dole bangarorin biyu su ɗauki matakai na gina amincewa da juna.

Shaibani ya ce an dakatar da tattaunawar kan yarjejeniyar tsaro tun bayan fara yaƙin Iran, amma yana sa ran za a sake farawa nan ba da jimawa ba. Ya kuma ce an katse hulɗa tsakanin ɓangarorin biyu bayan da Isra’ila ta kai hari kan wani sansanin sojin saman Syria.

Gwamnatin Syria na fatan cimma yarjejeniyar zai kasance mataki na ƙarshe da zai kai ga janye Isra’ila daga yankunan Syria.

Shaibani ya yi kira ga Isra’ila da ta yi amfani da wannan “dama ta tarihi”, yana cewa “ƙofofin diflomasiyya” har yanzu a buɗe suke. Sai dai ya kuma nuna damuwa game da rashin amincewa da juna: