Jam’iyyar APC ta bayyana gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, a matsayin dan takarar Sanatan Gombe ta Arewa bayan samun kuri’u masu rinjaye a zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka gudanar a jihar.
Shugaban kwamitin zaben fidda gwani na APC a jihar, Mallam Labiru Musa Kafur, ya ce an gudanar da zaben cikin lumana da gaskiya a dukkan kananan hukumomi 11 na jihar.
Haka kuma, tsohon mataimakin kwamishinan ’yan sanda, Mohammed Ahmed, ya zama dan takarar APC na Sanatan Gombe ta Tsakiya.
Kwamitin ya tabbatar da cewa duk wadanda suka yi nasara sun cika sharuddan kundin tsarin mulki da na jam’iyyar APC domin tsayawa takara a zaben Sanata mai zuwa.