Hukumar Kwallon Kafa ta Italiya ta sake naɗa Roberto Mancini a matsayin kocin tawagar ƙasar karo na biyu, kwana guda bayan Andrea Pirlo ya janye daga takarar karɓar aikin.

Pirlo, wanda ake ganin yana cikin waɗanda za su gaji kujerar kocin, ya hakura da neman aikin. Hakan ya biyo bayan rahotannin da suka alaƙanta shi da wani kamfanin caca na Rasha.

A wani sauyi da ya shafi tawagar ta Azzurri, daraktan harkokin ƙwallon ƙasar kuma tsohon kyaftin, Paolo Maldini, ya yi murabus daga muƙaminsa.

Kujerar kocin ta kasance babu mai riƙe da ita tun bayan da Gennaro Gattuso ya bar aikin a watan Afrilu, bayan Italiya ta kasa samun tikitin shiga gasar cin Kofin Duniya.

Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Italiya, Giovanni Malago, ya ce Roberto Mancini shi ne mutumin da ya fi dacewa da jagorantar tawagar a wannan lokaci.

Haka kuma, an bayyana cewa Claudio Ranieri, wanda ya jagoranci Leicester City zuwa lashe gasar Firimiya ta Ingila a kakar 2015/2016, zai maye gurbin Paolo Maldini a matsayin daraktan harkokin wasanni na tawagar ƙasar Italiya.