Kwamitin Majalisar Wakilai mai kula da Ka’idar Daidaito ta Tarayya (Federal Character) ya yi kakkausar suka kan abin da ya bayyana a matsayin "ci gaba da yin watsi da ikon da Kundin Tsarin Mulki ya bai wa Majalisar Dokoki ta Kasa" daga shugaban Hukumar Haraji ta Kasa Dakta Zacch Adedeji.

Kwamitin ya kuma ba da umarnin dakatar da duk wani shirin daukar ma’aikata da NRS ke yi nan take, tare da yin barazanar amfani da Sashe na 88 da na 89 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya domin tilasta aiwatar da umarninsa idan shugaban hukumar ya ci gaba da yin watsi da umarnin kwamitin. Sashe na 88 ya bai wa Majalisar Dokoki ta Kasa ikon gudanar da bincike domin gano cin hanci, rashin inganci ko almubazzaranci a gwamnati, yayin da Sashe na 89 ya ba ta ikon tilasta bayar da shaida, gayyatar shaidu da kuma fitar da sammacin kama idan ya zama dole.

A taron da kwamitin ya gudanar ranar Laraba a harabar Majalisar Dokoki ta Kasa da ke Abuja, wanda Hon. Ahmed Idris Wase ke jagoranta, kwamitin ya ce wannan sabon mataki ya biyo bayan ci gaba da kin amsa gayyatar Majalisar da shugaban NRS ke yi.

Kwamitin ya bayyana cewa a cikin wata wasika mai kwanan wata 15 ga Yuli, 2026, mai taken "Bukatar Jerin Sunayen Ma’aikata da Gayyatar Halartar Taro", ya bukaci shugaban NRS ya gabatar da cikakken kuma sabunta jerin sunayen ma’aikatan hukumar. Haka kuma an gayyace shi ya halarci taron na ranar Laraba, amma bai bayyana ba.

Kwamitin ya kuma tuna cewa a cikin wannan wasikar ya lissafa wasu wasiku bakwai da aka taba aikawa shugaban NRS, wadanda ofishinsa ya tabbatar da karba. Wasikun sun hada da na 13 ga Oktoba, 2023; 7 ga Nuwamba, 2023; 14 ga Maris, 2024; 3 ga Yuli, 2024; 16 ga Yuli, 2024; da kuma 1 ga Afrilu, 2026, mai lambar NASS/HR/CT.40/03/14.

Kwamitin ya zargi shugaban NRS da kin mayar da martani yadda ya kamata ga bukatun da ke cikin wadannan wasiku duk da cewa ofishinsa ya tabbatar da karbarsu.

Rikicin da ke tsakanin Majalisar da hukumar ya shafi batutuwa da dama, ciki har da takaddamar da ta taso kan izinin daukar ma’aikata da Hukumar Federal Character Commission (FCC) ta bai wa NRS.

Kwamitin ya tunatar da cewa tun da farko ya umurci FCC da kada ta sake bai wa NRS wani izini ko rangwame kan daukar ma’aikata.

A taron na ranar Laraba, shugabar FCC, Hon. Hulayat Motunrayo Omidiran, ita ma ba ta halarta ba. A sakon da ta aika wa kwamitin, ta bayyana cewa tafiyar aiki da kuma rashin lafiya da ta biyo baya ne suka hana ta halarta.

Sai dai kwamitin ya ce wannan sabon rashin halartar nata ya biyo bayan wasu gayyata da wasiku na hukuma da dama da ba ta amsa ba, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, kuma ya sabawa ka’idojin rikon amana da ake bukata daga masu rike da mukaman gwamnati.

Kwamitin ya bayyana cewa bai wa NRS izinin daukar ma’aikata da FCC ta yi cin fuska ne ga ikon sa ido da Kundin Tsarin Mulki ya bai wa Majalisar Wakilai, tare da nuna rashin girmama ikon da al’ummar Najeriya suka dora wa Majalisar Dokoki ta Kasa.

Saboda haka, kwamitin ya sake bai wa FCC umarni da ta dakatar da duk wani aikin daukar ma’aikata da Hukumar Haraji ta Kasa ke gudanarwa har sai shugabannin hukumar sun bayyana a gaban kwamitin domin yin bayani kan matakan da suka dauka tare da bin tsarin sa ido da Kundin Tsarin Mulki ya tanada.

Hon. Wase ya ce Majalisar Wakilai ba za ta zuba ido ba yayin da hukumomin gwamnati ke zabar irin umarnin kundin tsarin mulki da za su bi. Ya jaddada cewa sa ido da Majalisar ke yi ba zabin hukuma ba ne, kuma ba abin da shugabannin hukumomi za su bi idan sun ga dama.

"Majalisar Dokoki ta Kasa ita ce muryar al'ummar Najeriya. Ikon sa ido da Kundin Tsarin Mulki ya ba ta ba na ado ba ne. Wajibi ne domin tabbatar da rikon amana. Babu wata hukuma, kwamiti ko jami'in gwamnati da ya fi Kundin Tsarin Mulki karfi ko ya fi karfin sa ido na Majalisa."

Kwamitin ya yi gargadin cewa ci gaba da kin amsa gayyatar Majalisar da jami’an gwamnati ke yi na kafa mummunan misali, yana rage amincewar jama’a da tsarin dimokuradiyya tare da raunana tsarin daidaita iko da tabbatar da doka wanda ke kare dimokuradiyyar Najeriya.

A karshe, kwamitin ya sake jaddada kudurinsa na amfani da duk wata hanyar doka da kundin tsarin mulki ya tanada domin tabbatar da bin umarninsa da kuma kare mutuncin aikin sa ido da al’ummar Najeriya suka dora masa.