Mayakan Houthi sun ƙwace iko da birnin tashar jiragen ruwa na Mokha (Mocha) da ke gabar Tekun Bahar Maliya a Yemen, a wani mataki da zai iya ƙara musu tasiri a kan mashigar ruwa ta Bab al-Mandab, wadda ke da matuƙar muhimmanci ga zirga-zirgar jiragen ruwa na duniya.

Rahoton Reuters, wanda ya nakalto jami’an gwamnatin Yemen, ya ce mayakan Houthin na ci gaba da samun nasarorin yaƙi a yankunan bakin tekun, ciki har da Dhubab, yayin da suke ƙoƙarin ƙara faɗaɗa ikonsu a kan gabar Tekun Bahar Maliya.

Bab al-Mandab na daga cikin muhimman hanyoyin jigilar mai da sauran kayayyaki tsakanin yankin Gulf da Turai ta hanyar Tekun Bahar Maliya da mashigar Suez. Ƙara samun ikon Houthi a yankin na iya ƙara barazana ga zirga-zirgar jiragen ruwa da kuma samar da makamashi a duniya.


Wannan ci gaba ya zo ne yayin da ake ƙara samun arangama tsakanin mayakan Houthi da dakarun gwamnatin Yemen da Saudiyya ke marawa baya, lamarin da ke ƙara tayar da fargabar komawar Yemen zuwa cikakken yaƙi bayan tsagaita wutar da aka cimma a 2022 ta fara wargajewa.

A gefe guda, Houthin sun kai hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan wasu biranen kudancin Saudiyya, ciki har da Khamis Mushait, Abha, Jazan da Najran. Aƙalla mutum 73 sun jikkata a hare-haren baya-bayan nan, a cewar ƙawancen da Saudiyya ke jagoranta.

Hukumomin tsaron Saudiyya sun kuma bayar da sanarwar gaggawa a Khamis Mushait sau huɗu cikin sa'o'i 24, kafin daga bisani su sanar da cewa barazanar ta wuce.

Ƙaruwar rikicin na ƙara jefa shakku kan tsaron mashigar Bab al-Mandab, tare da yiwuwar yin illa ga kasuwancin duniya da jigilar makamashi idan tashin hankalin ya ƙara tsananta.